21 Yuli 2026 - 07:52
Source: ABNA24
Ambaliyar Ruwa A Afghanistan Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane Da Dama da Raunata Wasu + Bidiyo

Sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka yi da yammacin jiya Talata, 20 ga Yuli 2026 da kuma kwararar ambaliyar ruwa a garin Parun, cibiyar lardin Nuristan na Afghanistan, akalla mutane 20 ne suka mutu, 80 suka jikkata, kuma mutane 100 sun bace. Hukumar magance bala'o'i ta Afghanistan ta ce yayin da ake ci gaba da aikin bincike, akwai yiwuwar ƙaruwar adadin wadanda suka rasa rayukansu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) na Duniya – ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Hukumar magance bala'o'i ta Afghanistan ta sanar cewa sakamakon kwararar ambaliyar ruwa mai ƙarfi a jiya a garin Parun, cibiyar lardin Nuristan, akalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu, 80 suka jikkata, kuma sama da 100 suka bace.

Mohammad Yusuf Hammad, kakakin wannan hukuma, da sa'o'i kadan da suka gabata bayan aukuwar lamarin yayin da yake bayyana ƙididdigar ƙarshe na adadin wadanda ambaliyar ta shafa, ya ce sama da mutane 100 har yanzu sun bace, kuma akwai yiwuwar ƙaruwar adadin wadanda suka rasa rayukansu.

Faridoun Samim, kakakin gwamnan lardin Nuristan, a baya ya sanar cewa magajin garin Parun tare da wasu daga cikin masu gadinsa na cikin mutanen da suka bace.

Ya kuma kara da cewa ambaliyar ta yi barna mai tsanani ga ginin karamar hukuma, shaguna, gidajen zama, ofisoshin cibiyoyin sadarwa, da gadoji, kuma ta yi asarar kusan dala miliyan 36.

Jami'an Taliban sun jaddada cewa wannan ƙididdiga ta farko ce, kuma yayin da ake ci gaba da aikin bincike da tantancewa, akwai yiwuwar ƙaruwar adadin wadanda suka mutu da barnar da aka yi.

Ruwan sama mai ƙarfi ya fara ne daga misalin karfe 3 na yamma a jiyan a Parun da kauyukan da ke kewaye, wanda ya haifar da ambaliyar ruwa kwatsam.

Wannan lamari shine sabon misali na ambaliyar ruwa mai kisa a Afghanistan, wanda rashin ingantattun ababen more rayuwa da sauyin yanayi ke ƙara tsanantawa.

Dangane da rahotannin Hukumar magance bala'o'i ta Afghanistan, tun daga farkon shekarar hijira ta shamsiya ta yanzu (1405) zuwa yau, bala'o'in yanayi musamman ambaliyar ruwa da ruwan sama mai ƙarfi sun kashe mutane sama da 330 a Afghanistan, kuma sun raunata daruruwan wasu. Wannan ƙididdiga ta haɗa da abubuwan da suka faru a larduna daban-daban, kuma ta yi barna mai yawa ga gidaje, filayen noma, da hanyoyi.

…………….

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha